20/03/2025
Ramadaniyyat: 1446 [19]
Alƙur'ani Zalla ko Bijire wa Manzon Allah
4.0. Taƙaitaccen Tarihin Masu Ƙaryata Hadisai
4.5. Wasu Daga Cikin Jagororin Wannan Fitina: (4)
Ci gaba…
4. Alhafiz Aslam Jirajburi: Haifaffen yakin Azamgrah na ƙasar Indiya. An haife shi a shekara ta 1880. Ya haddace Alƙur'ani yana ɗan shekara tara, saboda haka ne ake masa laƙabi da Alhafiz. Ya karanci harshen Farisanci wanda shi ne yaren koyon addini a lokacin. Sannan ya karanci ilimin lissafi da harshen Ingilishi da harshen Larabci. Bai taɓa shiga wata makaranta ta zamani ba, ballantana ya yi karatun Jami'a, to amma saboda tsananin yadda yake son karance-karance sai ga shi ya kai wani babban matsayi a karatu.
Alhafiz Aslam ya zama marubuci a wata jarida mai suna (Baisa) wadda take fitowa kullum a garin Lahore. Wannan ne ma ya sa aka san shi a duk faɗin yankin Indiya. Sannan ya zama malami mai koyarwa a makarantar sakandare, inda ya koyar da harshen Farisanci da Larabci. Sannan a shekara ta 1912 ya zama mai tsaron ɗakin karatu (Librarian) a wannan makaranta wadda daga bisani aka ɗaga likkafarta ta zama Jami'ar Musulunci inda ya zama mai koyar da harshen Larabci da Farisanci a cikinta.
Sai dai kuma bai daɗe a wannan jami'a ba sai ya koma da koyarwa a Jami'ar Milliya ta Musulunci.
Abin da kuwa ya jawo Alhafiz Aslam faɗawa cikin aƙidar "'yan Alƙur'ani zalla" shi ne mas'alar rabon gado, yayin da ya karanta hukunci mai nuna cewa, ɗan ɗa yana hana baffansa watau ɗan'uwan mahaifinsa gadon dukiyar kakansa. Sai wannan hukunci ya taɓa masa zuciya, har ma ya ce, ya duba duk littattafan ilimin rabon gado bai samu wanda ya dace da ra'ayinsa ba, sai Alƙur'ni kaɗai ya goyi bayan ra'ayinsa, don haka ya saɓa wa wancan hukunci.
Alhafiz Aslam ya sami ƙulla kyakkyawar alaƙa da Ahmaduddin, ya kuma tasirantu da ra'ayoyinsa na ƙaryata hadisan Manzon Allah (SAW), har ma ya fassara littafinsa "Mu'ujizar Alƙur'ni" zuwa harshen Larabci, ya kuma yaɗa shi cikin ƙasashen Larabawa.
Alhafiz Aslam ya rubuta littafin "Mahjub al-Irsi" inda ya yi kakkausan s**a a kan hukunce-hukuncen Muslunci da s**a danganci gado. Hakanan kuma ya ɗosani wani ɓangare na ra'ayin 'yan gurguzu, wato na cewa, duk ƙasa mallakin gwamnati ce.
Alhafiz Aslam ya yi rubuce-rubuce masu yawa, ya kuma taɓo ɓangarori daban-daban. Ya yi rubutu a kan tarihin Musulunci da ɓangare Alƙur'ani da na Aƙida da sauransu. Kana iya cewa a cikin tafiyar masu ƙaryata hadisai kakaf, shi ne mutum na biyu bayan Barwiz, saboda yawan littattafan da ya rubuta don yaɗa wannan gurɓatacciyar aƙida.
Bayan kafa ƙasar Pakistan a shekara ta 1947 sai Alhafiz Aslam ya amsa gayyatar almajirinsa Barwiz, ya yi hijira zuwa Pakistan. To amma kuma bai daɗe a wannan ƙasa ba, sai ya sake tattara nasa ya nasa ya koma ƙasarsa ta Indiya inda a nan Allah (SAW) ya yi masa rasuwa a ranar 28 ga watan Disamba, shekara ta 1955 yana kimanin ɗan shekara 75 da haihuwa.
Za mu ci gaba in sha Allah…
Prof. Muhd Sani Umar R/Lemo ✍🏻